Hudubar Bankwana Mai Ratsa Zuciya Da Annabi SAW Ya Yi A Irin Wannan Rana Ta Yau Arfa

 




A irin wannan ranar ce 9 ga watan Zul-Hijjah, SHEKARA ta goma bayan Hijira a Dutsen Arafat (ranar Arfa kenan) Annabi Muhammad S.A.W ya yi wata huduba mai ratsa zuciya.


Fiyayyen Halitta (S.A.W) Ya fara da cewa:


“Ya ku mutane ku ba ni hankalinku, domin mai

yiwuwa ba zan sake kasancewa da ku bayan

wannan shekarar ba, saboda haka ku saurari

abinda nake gaya maku da kyau, kuma (ku isar

da abinda zan gaya maku) ga wadanda ba su a

wannan wuri a yau.


🎇

Ya ku mutane kamar yadda ku ka ri'ki wannan

wata, (na Hajji) da wannan rana (ta Arfa) da

kuma wannan gari (na Makka) da girma kuma

abin tsarewa, to, haka kuma ku riki ran Musulmi

da kuma dukiyoyinsu da girma abin kuma

karewa, ku maida wa mutane kayan da suka ba

ku amana. Kar ku cuci kowa, saboda kar wasu

su cuce ku. 


🎇

Ku tuna fa, hakika Allah zai yi

sakayya akan ayukakanku. Allah (SWT) ya hana

cin riba,(wato kudin ruwa) saboda haka, duk abin

da aka kulla ta kudin ruwa sai an warware shi.

Ku yi hattara da shaidan, domin kiyaye

addininku. Yanzu kan ya fidda ran batar da ku

akan manyan abubuwa (na sabo) saboda haka

ku guji binshi akan kanana.


🎇

Ya ku jama'a hakika kuna da hakki bisa

matayenku, amma su ma suna da hakki bisa

kanku, to hakkin su ne akan ku da kuciyar da su,

Kuma ku tufatar da su akan jin kai. ku bi da su

kyakkyawan biyarwa. Ku kuma tausasa musu

domin su majibintan al'amurran ku ne, kuma

mataimakan ku, Hakki ne akan su da kar su yi

abota da duk wanda ba ku so, kuma su nisanci

zina.


🎇

Ya ku jama'a, ku yi kyakkyawar bauta ga Allah

(SWT) ku tsaida salloli biyar (5) na farilla, Ku

azumci watan Ramadan, kuma ku bada zakka.

Ku aikata aikin Hajji idan har kun samu damar yi.


🎇

Ku sani fa, kowane musulmi dan uwan musulmi

ne. Dukkan ku daidai ku ke. Ba wanda yake da

fifiko saman wani sai wajen tsoron Allah da

aikata kyawawan ayyukka.


🎇

Ku tuna fa (ya ku jama'a) wata rana za ku tsaya

gaban Ubangijinku, domin sakamakon ayyukan

Post a Comment

Previous Post Next Post