Ma,aikatar wutar lantarki a Nigerian su shiga yajin aiki

 


Ƙungiyar ma'aikatan wutar lantarki ta Najeriya ta ce za ta tsunduma yajin aiki sakamakon cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi.

Ƙungiyar ta ce ta ɗauki matakin ne bayan da ƙungiyar kwadogo ta ƙasar NLC ta sanar da matakin tsunduma yajin aiki sakamon cire tallafin man fetur da gwamnatin ƙasar ta yi, lamarin da ta ce ya haifar da ƙaruwar hauhawar farashin kayayyaki a ƙasar.

Shugaban ƙungiyar mai lura da shiyyar birnin tarayya Abuja da Kogi, Godfrey Aba ya tabbatarwa da BBC cewa ƙungiyar za ta shiga yajin aikin daga ranar Laraba 7 ga watan Yuni, matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta janye matakin cire tallafin man ba.

Ya ƙara da cewa ''ƙungiyar za ta shiga yajin aikin ne har sai gwamnati ta janye matakin da ta ɗauka''.

A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sannun muƙaddashin sakataren ƙungiyar na ƙasar Dominic Igwebike, ta yi kira ga mambobinta da su yi biyayya ga matakin ƙungiyar na tsunduma yajin aiki a tsakiyar makon da ke tafe.


Source:bbchausa

Post a Comment

Previous Post Next Post